Daga - Mahadi Tukur Almizan
Daga Asubahi zuwa dare na jiya Asabar aƙalla Palasɗinawa 100 suka rasa rayukansu ciki har da masu aikin bada agaji da ƴan jarida.
Aƙalla Palasɗinawa 40 suka yi shahada a wani hari da Isra'ila ta kai inda Palasɗinawa sama da 100 suka samu mafaka a Tel al-Zaatar dake arewacin Gaza.
👉
BREAKING: Over 40 Palestinians have been killed in an Israeli airstrike targeting the home of the Al-Araj family, which was sheltering dozens of displaced people in Tel al-Zaatar, northern Gaza.
— Quds News Network (@QudsNen) November 30, 2024
Many are trapped under rubble, with rescue efforts hindered by a lack of Civil… pic.twitter.com/Uh3MTKfBK3
Kafafen yada labarai na cikin gida sun bayyana cewa haryanzu akwai mutane da suka maƙale a baraguzan gini saboda ƙarancin ma'aikatan hukumar agaji ta Civil Defense.
Hakanan an samu rahotannin faruwar makamantan wannan hari a Jabalia da Beit Lahia dake makotaka da arewacin Gaza, inda anan ma akwai mutane dayawa da gidajen su suka danne suna ƙarƙashin baraguzan gini tsawon kwanaki biyu da suka wuce, sakamakon hare haren Isra'ila.
Wancan harin na ƙarshe da Isra'ila ta kai zirin Gaza ne ya cika adadin shahidan ya kai aƙalla 100 a jiya kawai.
Tun da sanyin safiyar jiya Asabar ɗin ne sojin Isra'ila suka tarwatsa motar dake ɗauke da ma'aikatan ƙungiyar agaji ta "World Central Kitchen (WCK) NGO, inda suka kashe mutum 4 daga ciki.
👉
🚨Four WORLD CENTRAL KITCHEN’s workers have been KILLED in #Israeli_bombing of Khan Younis! pic.twitter.com/VboXCtodKp
— Motasem A Dalloul (@AbujomaaGaza) November 30, 2024
Ƙungiyar ta WCK suna sanar a jiya Asabar ɗin cewa za ta dakatar da ayyukan ta a Gaza a karo na biyu a cikin wannan shekara, kamar yadda ta yi a watan Afrilu lokacin da jirgi maras matuƙi na Isra'ila ya jefa ma motar su Bom wanda ya kashe ma'aikatan su da dama na ƙasashen waje.
Har wayau an sake samun rahoton wasu hare haren Isra'ila a Zirin na Gaza, kamar harin da suka kai Khan Younis dake kudanci inda suka kashe Palasɗinawa 17, ciki har da ma'aikacin ƙungiyar agaji ta 'Save The Children' Mai suna Ahmad Faisal Isleem al-Qadi tare da matar shi da ƴar su mai shekaru 3.
👉
Gaza | massacres
— Younis Tirawi | يونس (@ytirawi) November 30, 2024
13 Palestinians killed in an Israeli airstrike on Kaheel family’s home in Rimal area in Gaza City
In Shujjaiya, at least 10 killed on Rajb family’s home
Beit Lahia, 3 killed in a drone attack
In Khan Younis, 11 were killed while receiving flour bags pic.twitter.com/ir2fe1Znsv
Hakanan kuma sojin na Isra'ila sun kashe ɗan jarida ma'aikacin gidan talabijin na Al-Aqsa Tv mai suna Mamdouh Qunaita a wani hari da suka kai asibitin 'Baptist Hospital' dake kudancin Gaza da jirgi maras matuƙi.
