Offline

Sayyid Ali Khamenei ya gana da shugaban 'yan gwagwarmayar Islamic Jihad na Palestine.

 


Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Ayatullah Sayyid Ali Khamenei, ya yaba da nasarar da kungiyar Jihadin Islama ta Falasdinu ta samu a baya-bayan nan kan Isra'ila, yana mai cewa Ƙaruwar karfin kungiyoyin gwagwarmayar Falastinawa shi ne jigon durkusar da gwamnatin mamaya.


Ayatullah Khamenei ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ya yi da babban sakataren kungiyar Jihad Islami ta Falasdinu Ziad al-Nakhaleh tare da tawagarsa a birnin Tehran ranar Laraba.


A ranar 9 ga watan Mayu ne gwamnatin Tel Aviv ta kaddamar da hare-haren bama-bamai a Gaza, lamarin da ya haifar da harba rokoki sama da 1,000 da kungiyar Jihad ta Islama ta yi kan Isra’ila.


Daga bisani bangarorin biyu sun amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a shiga tsakanin Masar bayan shafe kwanaki biyar na fafatawa, wanda yayi ajalin falasdinawa 33 a Gaza ciki har da yara shida tare da raunata 147, a cewar ma'aikatar lafiya ta Falasdinu.


Isra’ila ta kashe kwamandojin Islamic Jihadi da dama a rikicin na baya-bayan nan.

Post a Comment

Previous Post Next Post