Offline

YADDA MARTANIN HARE-HAREN IRAN GA ISRA'ILA A JIYA,YA DACE DA RANAR DA IMAM ALI (AS) YA HALAKA AMRU BN ABDUL-WUUD A YAKIN KHANDAQ.

 



Kai harin Iran a ranar Lahdi 14/Naisan/2024-5/Shawwal 1445hiriyya;ya da ce da ranar ranar da aka yi yakin Ahzab/Khandaq tsakanin sansanin Manzon Allah (s) da kabilun Larabawa hade da hadin guiwar Yahudawa.



A ranar ne dai Imamu Ali (as) ya yi fito na fito da Shugaban Jaruman Larabawa da Yahudawa (Amru bn Abdul Wuud Amiriy) ya kashe shi.Manzon Allah (s) yana cewa:"Imani gabadayansa ya fita zuwa Kafirci gabadayansa.A sad da ya kashe (Imam ya kashe Amru) sai Manzon Allah (s) yace:"Saran da Ali ya yiwa Amru a ranar Khandaq daidai take da ibadar Saqalaini (Mutum da Aljan)"



Allahu Akbar! Izza tana ga Allah da Manzonsa da Muminai.


Naqaltowa:Ammar Muhammad Rajab


Fassarawa:Yusuf Kabir


Lahdi:14/4/2024.

7:31am.

Post a Comment

Previous Post Next Post