✍️ Mahadi Tukur Almizan.
Babbar hukumar lafiya ta duniya 'World Health Organization' ta yi Allah wadai da mummunan harin Isra'ila kan sansanin ƴan gudun hijira a Gaza da yayi sanadiyyar shahadar Palasɗinawa 70.
Wannan bidiyon da aka wallafa a shafin X wato Twitter ya nuna yadda ake zato mutane daga baraguzan ginin da aka kaima
WHO ta samu rahotanni masu tada hankali daga ma'aikatan lafiya dake aiki a Gaza na irin matsanancin halin da harin ya jefa mutane shugaban hukumar lafiya na majalisar dinkin duniya Tedros Adhanom Ghebreyesus ne ya bayyana haka a ranar Litinin a wani saƙo da ya wallafa a shafin X wato Twitter.— WATCH: Palestinians’ attempts to extract the wounded from under the rubble due to IOF warplanes bombing residential buildings in Al-Maghazi camp.
— Arya - آریا 🇮🇷 (@AryJeay) December 24, 2023
We’re 2,5 months into the war and israel has not yet stop bombing civilians. pic.twitter.com/qIBixu8zO1
"Akwai yaron da ya rasa gaba ɗaya dangin sa, hakanan shi ma wani Nurse ya rasa nashi dangin, duk an kashe su".WHO today visited Al-Aqsa Hospital, where scores of injured people were taken overnight following strikes in central #Gaza, including in the vicinity of the Maghazi refugee camp.
— Tedros Adhanom Ghebreyesus (@DrTedros) December 25, 2023
Palestinian health authorities reported that 70 people were killed, while Al-Aqsa Hospital staff… pic.twitter.com/B5503C82CT
Wannan magana ta Tedros ya biyo bayan kwana ɗaya da wancan mummunan hari na Isra'ila a sansanin al-Maghazi da ke tsakiyar Gaza.
Tedros ya ƙara da cewa "Hukumar lafiya ta Palasɗinawa ta bayyana cewa mutane 70 suka rasa rayukansu, yayin da jami'an lafiya na asibitin Al-Aqsa suka bada rahoton cewa aƙalla mutane 100 suka samu raunuka".
"A halin yanzu dai asibitin na kula da marasa lafiya fiye da yadda ma'aikatan su zasu iya baiwa kulawa".
" Dayawa ba zasu tsira ba" Tedros yayi gargaɗi kuma ya ƙarfafa cewa wannan mummunan harin ya ƙara nuna dalilin da yasa muke buƙatar a tsagaita wuta a Gaza.
A wannan bidiyon kuma an nuna ya irin barnar da wannan harin yayi ka rushe rushe
Tedros ya bayyana cewa WHO tayi matuƙar damuwa kan irin matsanancin halin da ake ciki a asibitoci a faɗin Gaza da suka rage ana aiki, wanda su kansu da suka rage sun kusa durƙushewa.🛑دمار كبير بمنازل في مخيم المغازي وسط قطاع غزة؛ جراء قصف الاحتلال.
— Suribelle 🔻 (@Syribelle) December 27, 2023
Major destruction to homes in Al-Maghazi camp in the central Gaza Strip As a result of the Israeli occupation bombing pic.twitter.com/aVCqgocbgk
©️ Freedom Fighters Ng

