Offline

Shekaru 7 da Suka Gabata: Yadda Mabiya Shi'a Almajiran El-Zakzaky Suke Aikin Ginin Cibiyar Su ta Husainiyyah a Zariya

A ranar Talata 10 ga watan Fabarairu,  2015, Mabiya Malam Zakzaky suke ta aiki a cikin muhallinsu Husainiyyah Bakiyyatullah,  Zariya,  an kammala wannan aiki da aka dauri aniyar yi a wadannan kwanaki.  Sai dai kuma daga zuwa  lokacin kadan sun ci gaba.  

Masu aikin sun hada matasa masu karfi a jika, da yara kanana.  Da kuma Manyan mutane.  Duk wanda ka tambaya,  zaka ji shi ya kawo kan shi wajen wannan aiki domin yin tarayya wajen gina wannan muhalli.  
Sai dai a tun daga ranar 12 zuwa 14 ga watan Disambar shekarar 2015 biyo bayan wani mummunan hari da Sojojin Najeriya suka yi a wajen inda aka kashe mutane da daman gaske, daga ƙarshe an rushe gurin gaba ɗaya ya zama Kango.

Post a Comment

Previous Post Next Post